Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Hajiya Dr. Asma’u Inuwa Yahaya Ta Kaddamar Da Yakin Neman Shigar Da ‘Ya’yan Da Ba Su Shiga Makaranta Ba
Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Hajiya Dr. Asma’u Inuwa Yahaya, ta kaddamar da yakin wayar da kai domin rage yawan ‘ya’yan da ba sa zuwa makaranta tare da fadada damar samun ingantacciyar ilimi a fadin jihar.
A lokacin bikin kaddamarwar da aka gudanar a Gombe, Uwargidan Gwamnan ta bayyana ilimi a matsayin mafi inganci wajen karya tarkon talauci da kuma gina al’umma mai albarka da ci gaba.
A cewarta: “Babu wani yaro da ya kamata a bar shi a baya. Ilimi ba kawai hakki ba ne, shi ne gindin kafa damar samun makoma mai haske ga ‘ya’yanmu, al’ummarmu da kuma jiharmu mai daraja.”
A cikin shirin, Gwamnatin Jihar Gombe ta bada tabbacin bayar da tallafin kudi ga makarantun firamare 50 da za su yi kokarin dawo da yaran da suka bar makaranta. Wannan, kamar yadda ta bayyana, zai zama karin karfafa gwiwa ga makarantu da al’umma domin baiwa ilimi mai shigar kowa muhimmanci.
Shugaban Hukumar Ilimi Bai Daya ta Jihar Gombe (SUBEB), Alhaji Babaji Babadidi, ya yaba wa Uwargidan Gwamna bisa jajircewarta wajen jagorantar wannan yunkuri na ilimi. Ya tabbatar da cewa SUBEB zai kara azama wajen wayar da kan al’umma, shiga zukatan jama’a da kuma fadakar da iyaye domin tabbatar da cewa kowane yaro ya samu damar karatu.
A cewarsa: *“Wannan yaki na zuwa a kan gaba domin taimaka mana mu kai ga yara mafiya rauni. SUBEB zai hada hannu da iyaye, al’umma da abokan cigaba domin tabbatar da cewa idan yara sun shiga makaranta, za su ci gaba da zama har su kammala karatunsu.”
Haka zalika, Shugaban shirin (UBEC) ya jinjinawa wannan shiri, inda ya bayyana cewa ya yi daidai da kokarin Gwamnatin Tarayya na rage yawan yaran da ke zaune a gida ba tare da shiga makaranta ba.
A nata jawabin, Kwamishinan Ilimi ta Jihar Gombe, Dr. Aishatu Maigari, ta sha alwashin cewa ma’aikatarta za ta bayar da cikakken goyon baya ga shirin, tana mai jaddada cewa ilimi shi ne ginshikin cigaban dan Adam a jihar.
Shima, Shugaban Karamar Hukumar Gombe,Barr Sani A.A.Aliyu ya sake tabbatar da shirin hukumar wajen gudanar da wayar da kai a matakin al’umma domin tabbatar da cewa iyaye sun rungumi wannan yunkuri na shigar da ‘ya’ya makaranta.
Babban abin da ya kayatar a wajen taron shi ne yin rajistar yara ta alama da Uwargidan Gwamna tare da sauran manyan baki, wanda hakan ya nuna kaddamar da shirin a hukumance a fadin Jihar Gombe.
Uwargidan Gwamna ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da jagorantar yunkurin tabbatar da cewa ilimi ya zama kayan karfafawa, cigaba da kuma sauyi mai dorewa ga rayuwar ‘ya’yan Jihar Gombe.
Zahrah Umar Adamu
Babbar Mai Taimakawa ga Gwamnan Jihar Gombe,
Ofishin Uwargidan Gwamna.
Comments
Post a Comment